BARAM-BARAM

BARAM-BARAM

Annabi na sonka nake

Kana ƙin mai ƙin nake


Nai bara'a ba ni sake

Izgilancin nan da suke


Sun yi zane sunka sake

Intanet can sinka fake


Dauri anyo Dandarake

Mai ƙafafun fanfalake


Yau ko hoton nan da suke

Ya yi muni kar mu sake


Ga tokobi nan a rƙe

Wai fa Islam yanda ya ke


To Muhammadu sun yi sake

Ya fi taurarin falake


Kyansa ya wuce duk ku riƙe

Kwarji ne ga hasike


Sanda Hassan yai kasake

Ya ga kyawu kyan gaske


Maimakon zambon da ya ke

Sai ya hau bege ya dake


Darajoji gun sa suke

Martabobo shi ya riƙe


Hassadar nan duk da ku ke

Ba ta tauye yanda ya ke


Wanga yaƙi ne da ku ke

Ku da Al-ƙahharu ku ke


Faɗuwa ce har a tuƙe

Ba bu riba duk ku riƙe


Duniyar nan ba ku sake

Ƙuntata ce har a tuƙe


Lahira wuta za'a sake

Ƙarƙashin Saƙara a niƙe


Izgilancin duk da ku ke

Bai na da can wanda ake


Ran Badar duk anka sake

Rijiya ɗuk anka ɗake


Babu wadi don ku fake

Koko tsauni har a tuƙe


In Ta'ala za ya riƙe

Tsanani damƙar sa ta ke


Na Samudu da Adu su ke?

Ƙaumu Lufin duk ya niƙe


Har biranan nan da su ke

Sai alamu kai a sake


To faɗan da Ilahu ke ke

Ni bara'a ce fa na ke


In fa Manzo an ka tiƙe

Rabbana sam ba shi sake


Ma'idah Allahu ya ke:

Gun mutun silken sa ya ke


Can Bara'a zo ka riƙe

Tai bayani kan su cike


Masu cutarwar da su ke

Kam sa duk wuta za'a bake


Ai da sannu fa don ku tiƙe

Za ku san zancen da nake


Can a ƙarshen Hijri na ke

Son ma kawo har a tuƙe:


"Mun isar ma kar ka sake

Izgilancin duk da suke


Masu shirkar nan da suke

Za su san kam yanda na ke


Mun sani zancen da suke

Za ya sa ƙunci ka dake


Tasbihi, sujada ka riƙe

Har ka komo inda mu ke"


Jalla na san ba ka sake

Gyangyaɗi kai ba shi riƙe


To Muhammadu na ka yake

Na sani kishin sa kake


Yau muƙaman nan da ya ke

Ga fa kafircin da suke


Rabbi nuna kan na fake

Yanda duk ƙudirar ka take


Jalla gaggawa fa na ke

Na sani dakon su kake


Wanga talala da keke

Wata rana za ka riƙe


Na yi kuka har ma tuƙe

Don takaicin nan da nake


Ba takobi don na riƙe

Ba kwari kuma babu bake


Sai fa alƙalami na riƙe

Ni fa koyin nan da nake


Gun su Hassan kan ya fake

Har su Sinhaji da ya ke:


"jalla Sarki son ka nake

Ayyukana don ka nake"


Shi fa gurbi yanda ya ke

Ba ido ne kar ku sake


Na yi koyi ne ku sake

Don ba zan kai yanda suke


To a ƙarshe kan na tuƙe

Ga fa fatan nan da nake


Sa bala'i kan su sake

Don gidajen nasu niƙe


Har musibu ba yanke

Duk a sasannin da su ke


Rabbana roƙon ka na ke

Sa Zabaniya masu fike


Sui dirango duk faɗake

Kan dukan arnan su niƙe


Wanga zancen nan da nake

Bai buwayar yanda ka ke

.


In ko har shiryar su kake

Zuciya hannunka take


In fushin ka ya zo ka riƙe

Nai bara'a ba ni sake


Ya Muhammadu son ka na ke

Kana ƙin mai ƙin na ke


Rayuwa fansarka take

Har iyaye nawa suke


Duk kumatu na a jiƙie

Alƙalam ɗai ni na riƙe


Wanga ɗan waƙen da na ke

Sa ya zam kuɓutar mu ya ke


Ban da ƙarfin nan da ake

Kai hari koko a cake


Alƙalam shi kam na riƙe

Zan yaƙin har na fake


Ban siyan kayam da suke

Tanɗe-tanɗen nan da suke


Tunda dai bautar da su ke

Dukiya ce ba su sake


in ko har mun daina sake

Zai zamo karya su mu ke


Duk musulmiya anyi sake

Sai fa barci ba faɗake


Ba ƙasa ɗai ta mu d ake

Yanke hurɗa gun su ta ke


Mimbari huɗubar da ake

Sun cane zagin su ake


Wai a daina sun fa fake

Tunzurawa wai fa ake


Mustapha manzo fa ya ke

Ya yi zancen da na ke


yau hadisan nan da nake

Yin karatun na fa riƙe


Ga yawa tarin mu ya ke

Babu ƙarfi ɗai da mu ke


Tsintsiya taron mu ya ke

Babu ɗai sharar da mu ke


Ga dalilam yanda suke

Wanga ƙasƙancin da mu ke


Rayuwa burinta muke

Muttuwa tsoronta muke


Yaushe barcin zai faɗake

Don mu san izzar da mu ke


Koko sai Mahdin da ake

Yin kira ya zo mu sake?


Ya Muhammadu son ka nake

Kana ƙim mai ƙin ka na ke


Ya fi rana ya fi wata

Ya fi taurarin falake


Ya fi Yusufu har Balke

Kwarjin kyawunsa ya ke


Ba ma kusa yanda ya ke

Sai ka ce shi kan sa ya ke


Isgilancin duk da su ke

Muntaqim na nan a faɗake


Sai salatin nan da kake

Kai ta yi masa ba yanke

************************


Na'Annabi Tanko Bala Gabari

3/R.Auwal/1429 (AH)

11/3/2008

Digitalized on:12/9/2019

=26/ Safar/1445

Comments

Popular posts from this blog

MAWADDAH

Raina Fansar Ka