Posts

Showing posts from October, 2021

MAWADDAH

In kana jin fushi da anbaci Zahra Ko mijinta da Ƴan Tagwayen Yara Tofa malam ka je ka sauya dabara Don kwa tsatsa a zuciya ka tara Ya kamata mu saura duk kan tsari Don ƙiyayyar da kai da mai tattaki Kar ta sanya ka yin fushi da Ma'aiki Bai buƙatar kuɗin ku ko alkaki Sai mawaddah ga Ƴan Gida mai Tsarki Suratush-Shura je ka sumnin fari In watan haihuwarsa ma ya kama Babu kai ba faɗa da tada husuma Ƙungiyar ka daban da ta su kwa suma Za su ce baka son Uba gun Umma Shi fa Manzon mu ne Bashiri-Naziri To batu ne ake na ƙaunar Sidi Bugi ƙaimi ka sake tamke sirdi Tafiyar nan shigo ciki ba ƙaidi Bisa tsari kuje wajen Maulidi Inda hali ku shafa ma bandiri

Na Gwanaye

NAGWANAYE Jinjina gun Gwani Wali na Ilahi Nagwanaye mu gaida Abdullahi Dan Aliyu uban Aliyyu Kisa'u Shi da Asim da ma Gwana Zahra'u Zan yabo ne ga haziki na tilawa Duk ku huta ku zo ku daina adawa Shi ya zamto ina kira kahuhu Ai Gwani ne mu gaida shi Na Ilahu Shekaru shidda sun riga sun fece Dalibai har rabin dari suka dace Sunyi saukar da ba'a ce ta dabino Sai ku kauce fa mahiran sun danno Rabbana shi kadai kawai zai saka Wanga aiki na juriyar nan taka Don Gwani yayi hankuri kan yara Har ya zamto fa dalibai  ya tara Ba shi kaushin hali da zai kore  su Sai kwa jinkai da tausayi domin su Dalibi gun Gwani Kabir Ya'kubu Ga Gwani mai yawan kwami ba aibu Har ijazah mutum biyar aka baiwa Ba dukan dalibanga ne su ka kaiwa Darajar ta ku gane mai girma ce Ba'a samun ta sai kwa an tantnace Sannu gwarzo da kwaikwayon Minshawi Da  Huzaifi kamar na ce masa rawi Ni ina sonka ya Gwani Abdullah Don tilawarka sai kwa masha'Allah Don qira'a bakwai...

HAIHUWAR DAN SUWAIBA

Bismillah jalla Rabba Yau batun nan zani duba Samuwar Manzonga Babba Ɗan Kinanata Ɗan Kilaba Mustapha na Khadija Babba Yau abin ba ƙanƙani ba ne ba Haihuwar da gun Suwaiba Duniyar nana ba taɓa ba Anga manyan al'ajubba Duniya ta sami Babba Lale da zuwan ka ya na Garba Tunda Allah yai halittar Adamun tun babu matar Yassako haskenga tartar Kan tsatson haularsa totar Koda ɗai ba'a sami tuntuɓe ba Yattawo ya zuwa ga Shisu Har ga Nuhu zuwa wasunsu Mudrika har illiyasu Ga Kinanata ga Kuraisu Nan ga Hashimu tunda bai ɓice ba Haskenga yana gusuowa Har ga Abdullah na baiwa Anyi auren ƴar budurwa Amina dangin muruwwa Sai fatauci yarriƙe shi Baba Nan da ƙare cin amarci Ya wuce domin fatauci Sai a dawowa ya tsinci Hanya ta Madina yacci Sa'i bai sami zakkuwa ba Sannu Amina sannu Giwa Duk ta mataye na baiwa Wanga aiki kin iyawa Kin dakon tunjum ga kowa Ki bushara ƴa ga Wahbi Babba Tunda taɗɗauke s...

Bushararru Goma

Bismillah zan jero sahabbai goma Da akai bushara kan rabo mai girma Allahu ke unguo da kaine mai rabo Watao Ma'aiki ko ka ce masa Shayabo Shi yai rabon aljanna gun wasu sabiqoon Su har guda goma kuce musu muttaqoon Acikin hadisin ya fade su daki-daki Domin zuwa kabarin su zan tattaki Su Abubakar da Umar da Zunnuraini Usmanu sai Zaki uban su Husaini Da Zubairu Dalha sai ka sa Dan Aufi Sai Dan Abi Waqqas Sa'ad mai karfi Da Abu Ubaidata sai Sa'eed Dan Zaidu Na wajen Wuraiqata kunji yan tauhidu Su ne fa farkon muminan doron kasa Da Rasulu yai shela ya zam sun amsa Allah dubun tsira a gun Al-Mujtaba Yardar ka karo kan sahabbai yan gaba

INA SON MUSTAPHA ALAI DA SAHBA

INA SON MUSTAPHA ALAI DA SAHBA Ina son Mustapha Alai da sahba Da matayenSa tsarkaka na duba Da masu biyar su ba zan rarrabe ba Tsare ni da ƙin su ya Allahu Rabba Inai muku aɗdu'a ya Sabiqoona Na Lansaru da ma na Muhajiruna Gwarazan nan na Badru da kau Hunaina Shahidan nan na Uhdu ba zan bari ba A wane ni da zan shiga zantukan ku Da Allah yaccane ya ma jiƙannku A saɓanin da yaffita nan cikin ku Fa ba ni da ɓangare balle na gaba Cikin nan na su zaɓaɓɓunga goma Da Ahlu Badar da Uhdu sunada himma Da masu mubaya'ar nan masu girma Fa yardaddu su ke gun Jalla Babba Ilahu da kanSa yazzaɓe su jumla Ga Manzo duk ciki ba mai fa illa A Attaura sifar su kaza Lijila Kira mai ƙin su arne ba da wai ba Gafuru jiƙan waɗannan ƴan uwan mu A imani fa su suka sha gaban mu Ka yaye dukka gilli zuciyar mu Ra'ufu Rahimu amsa don Suwaiba

MUHAMMADAWA MASOYA ALLAH

MUHAMMADAWA Muhammadawa masoya Manzo Allah ƙara kusanci sosai Basmalah zan faro bege Rabbana samin kyan hange Na fito dantse na zage Baitukan sui tsari jubge     Agaza Mahaliccin ƙassai Gaisuwa da salatai jingim Kan Ma'aikin nan mai tinjim Kausara ba mai sha lazim Sai masoyi gun Ɗan Hashim     Sha'iranga da ba sa yasai Zanyi waƙen kan ku masoya Masu begen shauƙin koya Ayyukan magabatan dunya Masu begen Ɗan Sa'adiyya    Na ga har da mutanen Wasai Jinjina a gareku matasa Harda manyan ba sa fasa Baituka gun angon Hafsa Safiya da dare  ba wasa    Gun yabon sun dage sosai Sun fito da muƙaman Manzo Kariya ma nan sun ƙwazo Shubbuhohin yaye hazzo Mu'ujizoji su ma sun zo     Kan yabo na sa sam ba kasai Rabbi shi ɗaya zai sakanta Hiddimar da ku ke wa Binta Ga mijinta da ma Abbanta Har sahabbai  ba banbanta    Duk ciki ba kanwar lasai Wa...

KAINE NA KE SO MUJTABA

Amshi: "Kaine na ke so Mujtaba Na san ba zan tozarta ba" Duk rayuwata kai na ba Fansa gami da uwa uba Har dukiyata zan zuba Domin na ceto Shugaba    Manzon da banga kamarsa ba Harshen ba zai iya furta ba Hatta rubutun nan gaba Bege kawai na saka gaba Duk lokutana kai na ba    Domin na sami wuƙar gaba Nan duniya da gidan gaba Ni kai na ƙe son zan yaba Ba ayyuka ne nayyi ba Saidai kawai ƙaunar da ba   Ta misaltuwa ya Shugaba Shin me ya sa ban gan ka ba Ga zuciya na fargaba Sai faɗuwa kullum gaba Ni banda kowa Jagaba    Sai so wajenka Mujittaba Ita zuciya na nan gaba Da dukan fa wanda ta sa gaba Kai narriƙe gam Shugaba Na zam maraya ba uba    Na san ba zan tozarta ba

SUBHANAKA ALLAH

SUBHANAKA ALLAH WITIRI Subhanaka Allah Wittiri Absa sabonsu mutan gari Fa bara'a ta ce zahiri Karbeta ka yi mini hanzari Kan aikin wawayen biri Allah shi yayyi samaniya Da kasa da dukan na tsakaniya Ba abinda ya ke da kamanniya Da Ilahu makagin duniya Mai ji da gani ne Zahiri Allah daya ne duk mun sani Shi ne kudurin duk mumini Duk wanda ya ke daukar wani Matsayin Allahu Muhaimini To ya bata hanyar Fadiri Yan hakika masu fagabniya Wai komai Allah don tsiya Ku sani hanyar durkaniya Ku ka kama ga hauragiya Qul huwallah Allah Wittiri Subhanaka Allah Mai Sama Sabon da su ke ya girmama Ma su karyar bi gun Barhama In sun ki su daina sun sama Tsine musu Allah Qadiri Dukkan taklifi kun ki yi Wai kunyi fana'i ba ku yi Sallah da ibadar Muhyi Kun kauce dukkan wahhayi Addinin bogi ku ce giri Har zagin Allah ma su ke Bin mata har da giya su ke Sha ba kunya don sun sake Fa akidar sai yado take Rusa Gwani don zikkiri Subhanaka Rabbul Izzati Amma yasifoona ...

SANYIN IDANIYA

SANYIN IDANIYA Ganin Sidi shi zai bani sanyin idaniya Mafarkinka shi ne nawa buri a duniya A duk randa nassan wanga sa'a da safiya Fa zan fara albishiri da murna da dariya Idan na mace ranar fa Sam ba haya niya Gama an cikan burin da ke rai guda daya Aya Sidi mai sona ina kara godiya Bisa son da kai min wanda ka zarce ma iya A sallah ka ke samun sa sanyin idaniya A begenka ni zan sami nawa gaba daya

MU TSARKAKE ALLAH

Ku tsarkake Allah dai ku dawo ga gaskiya Ka dauki batun nan in ko ka ki shi sai wuya Ina tsarkake Allah da siffar da sun masa Su na kirkirar karya ga Sarki na duniya Fa Allah guda ne ba uba bai da ko ɗiya Kini baida shi Allahu ne Kwal guda ɗaya Ina mai hakika mai kiran kansa wahidun Tuno dulmiyar Fir'auna kogi na Maliya A yayinda yacce wai azo har a yi masa Fa bauta a kyale Rabbu sarki guda daya Kadaita ta Allah ba mu shakkar ta kun sani Ina yan hakika masu kagenga yan tsiya Ku ce la sharika lahu a suna da ma sifa Da duk ayyukan Allahu ya Mai Dawainiya A Al'arshi Allah ya fa daidaita kun jiya Irin yadda yaddace da zatinsa shi daya Kace wai akwai Allah cikin dukkanin jiki Tajallin da kai zance fa karya ta yan giya Fa ba bu abin bauta da gaske kamar huwa Huwallahu Al-hayyu fa Sarkin da yattsaya Idan zaka shekara yin ibada cikin duhu Na halwa ka san ba za ka zam Rabbu ko daya A babu wusuli ba fana'i fa ko daya Ana yaudarar yara da daidai da daidaya Su...

TSABGAR HAƘIƘA

TSABGAR HAKIKA Tsabga na dauka nai nufin zan tafka Kan ja'irannan masu yinta hakika Zan doki kan duk mai uba har shege Bauta ga Allah in yanai da hadaka Subhana Allah bai kini ko dangi Sarki Gwani wannan da ba shi da tamka Allahu dai ne ba batun yin shirka Tilo, guda, qwal kansa ba ma shakka Alfardu ya aiko da duk manzanni Da riko ga rauhidi  a bar wata harka Kakan mu Nuhu da yai ta faman da'awa Kan masu bautar  Wadda harda Ya'uƙa Yai shekara curin dubu ba hamsin Yana ta fama don su bar yin shirka Ita kaddara kullum ta na kan fata Ambaliyar Ɗufana duk ta halakka Allahu ya aiko dukan yan sako Da nufin a bauta mas a daina hadaka Wai yau a al'ummar Masoyi Mujtaba An  samu shaidanun da sun fita zakka Guzma da sunka fake da harbin karsana Sun maida komai rabbu wai la shakka Sun maida zagin Jalla ma wata sara Lokon Afawa Mustapha su ka taka Sun haukace tuburan a wanga akida Don yayi nisa mai kira bai jin ka An ba su wurdin bogi wai na wusuli...

MUGUN BAWA

DAN HAKIKA MUGUN BAWA Dan Hakika mugun bawa jakin banza la'ananne Mushriki ne ko yai sallah Ga dan farka tonanne Masu zagin jalla wa'azza Harda Manzon dukka mutane Kafiri ne tsantsa wallah Ya rike komai Allah ne Babu sallah babu salati Sai tulin suma jaki ne Dan Hakika ka kaskanta Ja'iri mai doyin nan ne Da ina jin wai wai kunce Yau kazantar naji da kunne Ban raga muku ku yan iska Ni da ku yau ni ko ku ne Haihuwa tasa anyi asara Jakin banza tsinanne Ba shi wanka baya wanki Kunga mai doyin baki ne Duguja sunanka a gun mu Fajiri mai bin Rasta ne Ko Buraiman naku ku gane Ya sani bawan Allah ne Ya fada shi mai bauta ne Gun Ta'ala duk fa ku gane Banda kai banzar bazara ne Zaka ce komai Allah ne Duk ku tuba ku bar yin shirka Wanda yakki ko dan banza ne Haihiwarka fa gwanda barinka Ja'iri mai jahilci ne Jinjirin jaki ya fika Tunda shi mai tauhidi ne Mai hakika mugun bawa Jakin banza tsinanne

ƊAN HAƘIƘA KA HALAKA

Dan hakika ka halaka Mulhidi ne kar ku sake Ya ki bin tauhidi yana Zantukan sabon da ya ke Rabbu ba zai barku haka Ayyukan shirka da kuke Ya cane komai da ya ke Duniya wai rabbu ya ke Ka ga soko dan wahala Hankalinka ina ya fake Ba abin bauta dunya Sai Ilahu fa kar ku sake Annabin karshen dunya Mustapha ManzonSa ya ke Babu laifi mai wahala Da ya kai shirkar da su ke Kunga Inyas bawa ne Anbaton Manzonsa ya ke Duk yawan zikrin da kake Sarmadan bawa fa ka ke Ba wusuli babu fana' Zantukan karyar da kuke "Duk abinda ya bar shari'a Ba tafarkin nan ba ya ke" Annabin Rahmar mu daɗa To gaban fa waninsa ya ke Zantukan Abdul Inyas Har ga yau rudani su ke Mustapha Manzon mu yake Rayuka fansarsa mu ke Babu shaidanin da mu ke Sauna in zancen sa ake Ya kamata ku tuba ku san Annabin ma ta fa fake Sanda duk Manzon ka taɓa Mai gidanka fa za mu dake

BEGENKA HAMIDU

Allah ina kauna a gun Manzona Sanya ya so ni da dukkanin dangina Da dukan masoya ma su jin begena Sa duk musulmi ban rage kowa ba Kaunarka Ahmadu ta cika min zuci Ta ratsa loko sakuna duk ta ci Ta bar ni kullum ni da kukan zuci Allahu don kaunar ka shafe zunubba Na so ace na zo a tawagar Habsha Da su kai kidan nan wanda har Nanasha Ta fake a bayan na ka kallo ta sha Da na yi alfaharin da ba karami ba To yanzu zamunnan mu sun banbanta Sai dai ina begenka Baban Binta Kullum ya na kone da zuci da hanta Allah ka kai shi gaban sa ba don ni ba In nai salati gunka na san kaji Duk sanda nai dai Rabbi zai yi Odoji Zai ba ni lada goma ba wani canji Sallu alaihi wa sallimu ba wai ba Zan je ziyara Dausayin Aljanna Raudha na ke so don su ganka idona Kamshi na shabbakin ka ne burina Allah ka horen kar na kau ban je ba In na ji sunan ka na kan shiga hali Hali na jazaba ga shi ba ni da hali Inje ziyarar dan uwa ga Akili Manzo mijin Dija Uban Zainaba Duk masu begen Mustapha ...

TARBAR WATAN MAULIDI 1443H

  Tarbar Watan Maulidi 1443H Ya Rabbana ka kai ni nan da maulidi Domin na wasa Shugaban mu Ahmadi Na yo salati gunsa babu adadi Na je wajen tarurruka na maulidi Na yo yabo na harraka har da kidi Na watsa kyautukan turare da kudi Da tamburan yabo ga Sidi Ahmadi A bamu siratun-nabi Muhammadi Na kara sonsa koda yaushe da dadi Na dinga ba shi kariya gaba-gadi  Na samu walwala a rai ba adadi Na samu sirrukan yabo da madadi Na sake baitukan yabon kamar badi Na yo hawan sarakuna har da nadi Na sanya tagguwar kawar manyan kudi Ranar zuwansa Mustapha na ke fadi Ya Rabbana Raya ni nan da maulidi Don nai farin cikin zuwan Muhammadi Na Annabi Sanda 24/3/1443 2/10/2021