KANWAR LASA
KANWAR LASA Fa Walidan Manzon mu gagara gasa Ina yabon kanwar da ta wuce lasa Bismillah Allah ni na ke farawa Sarkin da shi ne dai na ke bautawa Baya azaba tun gaban aikawa Zan yo yabon Abdullah harma Giwa Fa Walidan Manzon mu Angon Hafsa Cecekucen ne ya ki yai karewa Wai duk akan Abbansa har Yar Baiwa Fa Amina yar Wahbi kin wuce kowa A duk matakai kunga sun tserewa Mai son ku shi ne yau na ke rarrasa Maganganu ba kan gado mun ji su A bayyane tun da ana boye su Akan makomar wai Iyayen Shamsu Wannan da shi ne yazzamo dawisu Ga duk ma'aika kunji dan Abbasa Yau na gaji shi ne na ke yin raddi Ga masu zance ba bu kai ba gindi Su na ta sukuwa sun hawa ba sirdi Ana ta zance kan Iyayen Hadi Wannan abin ya sa jini ya tafasa Ka na da riba in ya zamto ka ce Wannan karatun nan kamar ka zauce Kana fada harma kana wani huce A ranka gaba ko kiyayya dai ce? Ga Mujtaba Manzon mu raina fansa Wannan ya sa ma Audu yai tawaye Ya ce hadisan duk akwai jurwaye Ya...