Raina Fansar Ka
Ina ƙaunar Miji gun Nana Hafsa
Iyayena da kaina gun ka fansa
A sunan Rabbu Ƙhaliƙu ne na kan sa
Idan zan fara komai don isar Sa
Salat da salami ninninka akan sa
Da rahma har da albarka akan sa
Da mataye ka sa ahlin gidansa
Sahabbai har da masu biyar sahun sa
A bayan nan a yau zan nuna son sa
A waƙen nan idan na bada amsa
Ga mai neman dalilin nuna son sa
Da arna masu batanci akansa
Da fatan za su gane ina na dosa
Gama sam ba su gane kala ta sonsa
Muna ƙaunar sa ne ƙaunar da ke sa
Mu bar komai idan shi za ya nisa
Abu Sufyanu in na tuno batun sa
Da ɗai bai san ba wanda ka so kamar sa
A faɗin duniyar ga iya saninsa
Mutum bai so waninsa ba sam kamar sa
Sahabi ne ana cisgar jikinsa
Ya ce bai son ƙaya fa ta je wajen sa
Mu kan iya bada komai mu a kan sa
Iyaye duk da dangi kansa fansa
Riƙe al'ana ya Umari hadisa
A son sa ku sa dukan komai ƙasansa
Ku so shi ku bi shi ba mu da ɗai kamar sa
Mu kare shi da alayen gidan sa
Comments
Post a Comment