HAIHUWAR DAN SUWAIBA
Bismillah jalla Rabba
Yau batun nan zani duba
Samuwar Manzonga Babba
Ɗan Kinanata Ɗan Kilaba
Mustapha na Khadija Babba
Yau abin ba ƙanƙani ba ne ba
Haihuwar da gun Suwaiba
Duniyar nana ba taɓa ba
Anga manyan al'ajubba
Duniya ta sami Babba
Lale da zuwan ka ya na Garba
Tunda Allah yai halittar
Adamun tun babu matar
Yassako haskenga tartar
Kan tsatson haularsa totar
Koda ɗai ba'a sami tuntuɓe ba
Yattawo ya zuwa ga Shisu
Har ga Nuhu zuwa wasunsu
Mudrika har illiyasu
Ga Kinanata ga Kuraisu
Nan ga Hashimu tunda bai ɓice ba
Haskenga yana gusuowa
Har ga Abdullah na baiwa
Anyi auren ƴar budurwa
Amina dangin muruwwa
Sai fatauci yarriƙe shi Baba
Nan da ƙare cin amarci
Ya wuce domin fatauci
Sai a dawowa ya tsinci
Hanya ta Madina yacci
Sa'i bai sami zakkuwa ba
Sannu Amina sannu Giwa
Duk ta mataye na baiwa
Wanga aiki kin iyawa
Kin dakon tunjum ga kowa
Ki bushara ƴa ga Wahbi Babba
Tunda taɗɗauke shi ta san
Ba batu ne sam na wasan
Ƴan ƙananan yara kunsan
Bafa kanwa ce ta lasan
Ba macen da ta kai ki ba taɓa ba
Duk wata sai an bushara
Tun na farko har na tarra
Annabawa anka tara
Don tarar Abba ga Zara
Babu al'ajuban da bata gani ba
Har zuwa ga Rabi na farko
Nan a farko ne na mako
Nanga shashe shabiyun ko
Duniyar nana tayi bako
Wanda ba taɓa jinsa ko gani ba
Tun gabanin wanga hijra
Tun a Taura an bushara
Har a Linjil an kirara
Ahmadun ka faɗa ka ƙara
Har irin siffarsa ba rage ba
Aljanu da su kanyi tsani
Don zuwa sararin samani
Kan su sato ɗan bayani
Sunga sauyi yayi muni
Ba su san manufar Ubangiji ba
Shin azaba ce ta sauka?
Ko ko haske ne ya haska?
Duk kwa sambatu ya ɗauka
Ya zamo tamkar na hauka
Don shirin tarbarsa Ɗan Suwaiba
Ƙoramar nan mai ruwa fal
Ta ƙafe da zuwan na Naufal
Farisa da wutar su mai fal
Ta bice yau ba ta fal- fal
Haske ba za ya bar duhu ba
To gabanin wanga jewa
Anyi kissar nan ta giwa
Sanda arna sunka zowa
Ka'ba za sui bigewa
Wandaran bai bar su sun hakan ba
Shekarar giwa ta doko
Sammako kai anga iko
Jalla mai damƙa da dako
Haihuwarsa Rabi na farko
Anga haske wanda ba taɓa ba
Shekara ta ɗari biyar ce
Ƙara saba'in kayi dace
Haihuwar Isah fitacce
Ɗa ga Maryamu tsaftatacce
Da ga duk shirkar nasara duba
Can gabanin assubayi
Litinin haske da sanyi
Ya iso sujada yake yi
Kunji mai Sarki Buwayi
Amina bata santa naƙuda ba
Ya shigo dunya a wanke
Harda kwalli harda haske
Ba ƙazanta cibi yanke
Anyi shayi babu sake
Ɗahirun tsarki gareka babba
Nan da nan aka je bushara
Inda kaka nas ya dara
Nan ga Ka'ba an ishara
Ran Mutsallabi yassarara
Yai tukuici yai rabo da gumba
Take sau kwa gari ya ɗauka
Har kuyangar nan ta Makka
Gun Abu Lahbin ta sheka
Tai bushara nan ya sauka
Ta san ƴancinta ba musu ba
Yai tukuici nan na homa
Harda dabbobi da dama
Dukiya duk sai ya kama
Yin rabo don haihuwar ma
Ɗan uwa nasa wanda bai da rai ba
Sai Mutsallabi yarriƙo shi
Ka'aba ya tawo da shi shi
Yaɗɗaga shi ya ambashi
Jalla shi yabba shi kimshi
Ba'a san sunan a zamuna ba
Yakkira shi Abin Yabawa
Don ya sami yabo ga kowa
Nan ƙasa harma bisawa
Mai riƙon Tutar Yabawa
Ce MUHAMMADU ba da inkiya ba
Duk fasahar larabawa
Duk zalaƙar harda baiwa
Harda hikmar sun gazawa
Inkiyar da ka tanadarwa
Mustapha ba su san ta sun saka ba
Duniya ɗuk ta yi haske
Duk duhu kuma sai ya waske
Don zuwan Manzo na gaske
Shi jakada ne na yanke
Babu limancin da bai riƙe ba
Har a yau fa muna ta murna
Don zuwan rahmar nufina
Harda falalar Jalla guna
Shi ga dukkan alamina
Jinƙai ya zamo ba kui musu ba
Maulidi indai ya kama
Duk masoya sai kwa himma
Ai robon biskit da Lima,
Lukiraka har da ƙwai ma
Ba irin bidirin da ba mu yi ba
In kana jin kunci zuci
Har da zafi harda daci
In wata na Rabiyyu ya ci
To kwa imaninka binci-
ki fa kar ka barar ba kai awo ba
Dole mui fara'a da murna
Don busharar Dan Amina
Shugaban duk talikina
Da ga Adnan Shugaban na
Dangin mu ku zo mu daina gaba
To wajen yin maulidin nan
Sai a lura da tsarikan nan
Bin shari'a babu cudan-
Yar maza mata wajen nan
Bada yasassun batutuwa ba
Duk darajja har muƙamai
Ya riga ya sami dammai
Tunda shi yazzarce sammai
Ba buƙatar mui ƙirar mai
Ƙarya ɗomin ɗaga shi Babba
Duk halittu ba kamar sa
Mustapha Ango Na Hafsa
Duk muƙamai na wajen sa
Kui bushara masu son sa
Da rabon Firdausi ba ƙasan ba
Sai salati sallamawa
Kan fiyayyen Annabawa
Shugaban kowa da kowa
Mai riƙon Tutar Yabawa
Ran ƙiyama kunji ba musu ba
Godiya ga ubangijna
Wanda shi ne yai nufina
Yaccika min yau batuna
Haihuwar Manzo na Nana
Ba gumin goshi fa ban gaza ba
Ni Bashiru uban Humaida,
Garkuwa, Shu'aba ku shaida
Ni ina son mai Sujuda
Mujtaba ahlinsa harda
Duk sahabbai ban cire guda ba
Nan nake son zan taƙaita
Ba ni son dai tattsawaita
Tun Safar da can nayi ta
Haddatau yaɓɓalgace ta
Sai Rabi' na kuma ta ban gaza ba
Biyu ne dai to a farko
Maulidi farko a mako
Jalla har yabba ni iko
Naggama na saku dako
Allah sa ba don riyar na ke ba
Hijrar ta alif ka sanyo
Kan ɗari huɗu to ƙidanyo
Arba'in sai ukku goyo
Shekarar ce bata ɓoyo
Tarihin bai zamo ɓata ba
Ya zamo miladi dadai
Tara kan Oktoba ne dai
Shekarar alfaini saidai
Ashirin ƙaro da ɗai dai
Haihuwar Isah Nabiyyu babba
Ni Bashar jika ga Binta
Na zamo kwa mawallafinta
Rabbi shi ne yai nufinta
Shi ya sa kaima ka ji ta
Sallama ga Rasulu Ɗan Suwaiba
Godiya gun Jalla Sarki
Wanda yattare shi tsarki
Shi yasa nazzam mawaki
Gun Badaɗina Ma'aiki
Baiwa ce ba da fariya ba
Comments
Post a Comment