MUHAMMADAWA MASOYA ALLAH
MUHAMMADAWA
Muhammadawa masoya Manzo
Allah ƙara kusanci sosai
Basmalah zan faro bege
Rabbana samin kyan hange
Na fito dantse na zage
Baitukan sui tsari jubge
Agaza Mahaliccin ƙassai
Gaisuwa da salatai jingim
Kan Ma'aikin nan mai tinjim
Kausara ba mai sha lazim
Sai masoyi gun Ɗan Hashim
Sha'iranga da ba sa yasai
Zanyi waƙen kan ku masoya
Masu begen shauƙin koya
Ayyukan magabatan dunya
Masu begen Ɗan Sa'adiyya
Na ga har da mutanen Wasai
Jinjina a gareku matasa
Harda manyan ba sa fasa
Baituka gun angon Hafsa
Safiya da dare ba wasa
Gun yabon sun dage sosai
Sun fito da muƙaman Manzo
Kariya ma nan sun ƙwazo
Shubbuhohin yaye hazzo
Mu'ujizoji su ma sun zo
Kan yabo na sa sam ba kasai
Rabbi shi ɗaya zai sakanta
Hiddimar da ku ke wa Binta
Ga mijinta da ma Abbanta
Har sahabbai ba banbanta
Duk ciki ba kanwar lasai
Wanda yaiwa Ma'aiki zambo
Ko habaici sai sun ɗebo
Baituka zafafa zubbo
Kariya gun Manzo dubo
Na ga harda mutan Yakasai
Masu koyin Hassanun nan
Harda Ka'abu da Khansa sannan
Masu bin su a tsari kenan
Busuri da su Alfha ɗinnan
Har su Rabi'u Ɗan ƴan Ƙosai
Ga nasiha gunku fa zanyo
Shi yabo in dai za kai yo
To ka zam neman ilmi yo
Jahili ba zai yiwu yaiyo
Baitukan begen sui rassai
Shawara a gereku matasa
Gun yabo kar kuiwo wasa
Nan sani sannan sai ka sa
Wanke niyya kar kai gasa
Rabbi za ya biya can dausai
Duk abinda ka so zanawa
Nemi malam yai dubawa
In akwai gyara zai sawa
Baitukan ka su zam haskawa
Don ka tsira ga sharrin harsai
Jinjina ga masoya Manzo
Muhammadawa kunyo ƙwazo
Ko da marka ne sai kun zo
Masu shiɗewa don Manzo
Allah ƙara kusanci sosai
Rabbi karɓi dukan aikin su
Sha'irai da masoya na su
Sa a mizanin aikin su
Kuskuren su ka shasshafe su
Faɗiri Mahaliccin ƙassai
Sai salati gun Ɗan Baiwa
Shagaban nan mai yin baiwa
Wanda Allah shi yabbaiwa
Duk mukullan rahmar sawa
Jannatu lambun mai dausai
Shugabana Ango Hansai
Ni ina ƙaunar nan sosai
Ga shi ba ni da tsanin nan sai
Nan gare ku nake so in sai
Inda kai wahala an fissai
Comments
Post a Comment