ALLAH JIKAN MALAMI MAI QALA HADDASANA

Allah jikan malami mai qala haddasana
Sannan ka sa shi makotar Sayyidul Kauni

Ya sha wuya gori ka hada batun asali
A hakan ya sauke littafai harma Sahihaini

Farkon fadan sa da yan ilimin Hakika ne
Su ka zam kiransa da Ahmaq zantukan muni

An fara dagar da tsagin Qadirawa ne
Magana ta Sawi da yai gefen Jalalaini

Aka ce a maida shi Ghana wai na haure ne
Kuma wai aqidun sa sun sabawa Qur'ani

Duk wata kutungwuilar da sun kai ta zamo banza
Domin ya na nan da tanyon Jalla Ramhmani

Ya rayu kam kuma yai tsufansa mai kyawu
Kan burtalin sunna hakaza na Qur'ani

Yayinda Bawa na Inyas yayyi banbarma
Malam ya fede Hakika tunda tai muni

Su ka je wajen wani wai shi Tambari Yabo
Ba sa batun kare Manzo Sayyidul kauni

Ya fara da'awar nan tun a Bayero ne
Darul Hadisi ya koma don matsin tsanani

Alhamdulillahi Malam na yi ma barka
Da ka furfure kan hadisan da ga Adnani

Ya tarbiyar, ya zaburar sannan kwa ya koyar
Fanni na ilimin hadisi har da Qur'ani

Baiti na Larabci da kullum shi ya ke ta fada
Zan fassara ko zan iya to zo ka dan jini

"Duk wani sani in banda Qur'an na wofi ne
Sai kuma hadis hakaza sanin dini

Ilimi fa sai ya zamo kwai qala haddasana
Abinda ba shi ba rudi ne na shaidani"

Allahu Akbaru ga zance na mai hikima
Da Malamin mu ya ke zance ya na nuni

Ranar Ahad yai batun shi kam fa zai huta
Yai dariya yai sallama sam babu alhini

Ashe ashe hutu na Karshe shi ya ke dauka
Ba wanda yassan nufi nai ko ya yo auni

Yau Juma'a na ji ne can inda BBC
Malam fa ya tafi can izuwa ga Rahmani

Ranar hudu ga Jumada wadda ke sani
An tashi kai nai fa  kowa na ta alhini

Hijira ta forteen ka karo arba'in da uku
Bakwai Janairu twenty-two a Rumani

Allah jikan Malami mai qala haddasana
Duk ayyukan sa na khairi sa a mizani

Sannan ya tashi a gefen  wanda ke shauki
Manzo nufi na a gefen nasa Al-Ghani

Nai sallama da salatin wanda an baiwa
Qur'an da hikma ta sunna don ya yo nuni

Ni ne Na'Annabi mai begen masoyin ku
Allah jikan Amadun Bamba fa Al-Ghani

Comments

Popular posts from this blog

Raina Fansar Ka

BARAM-BARAM

Ya Rabbana raya mana Muhammada