GWANIN MAI KOYO

Bismillahi za na tsaro waƙa
Ta gwanaye ciki da 'Musan Gayya'

Yau ina alfahar da 'Musan Malam'
Ya zamanto gwani abin a kiyaya

Da ace babu masu koyo tabbas
Da gwani ya zamo abin jin kunya

Tun ya na ƙanƙani mu ke tatata
Ga kafafun sa sunyi ƙwari gaya

Na yi murna da ɗalibin yaffini
Ni kawai sai na ce da shi Ala raya

Ga fa Musa Rufa'i mai albarka
Haziƙin ɗalibi maso jin kunya

Ya kasance tsatson 'Karin Kundi' ne
Ga shi ɗa gun Rufa'i mai tarbiyya

In ka koma ta ɓangaren Barnoma
To gwanintar jinin su ne zurriyya

Rabbana sa ya zam na tsoron na ka
Kar ya zamto dugadugan sa su juya

Tsarkake zuciyar ka sa ikhlasi
Gun tilawa ka sa ya zam ba shi riya

Rabbana ƙara ba shi ƙarfin hadda
Don ya zamto gwanin da ba bu hamayya

Godiya gun Rufa'i jikan Hamza
Muqri'i ne a daina ma jayayya

Bai da aikin da yawwuce Qur'ani
Sa ya cece shi ran da duk za'a tsaya

Ba tijarar da taffi yin Qur'ani
Don kwa 'Ahlin Ilahu' ne nan dunya

Daga Anasun idan ka dau Dabara ni
Za ka gane batunga ba jayayya

Ba asara cikin ta sai dai riba
Da tukuici mafi yawan sakayya

Gun su Allah ya bar tsaron Qur'ani
Da tsarewar Sa sun zamo makiyaya

Rabbi ladan ka kai shi har ga uban mu
Marigayi Uba Gabari Na Yahya

Ya kasance mutum maso Qur'ani
Ga tukuicin Kareemu nan tun dunya

Malamin ya zubo wasiyya goma
Da ga shehin sa ne Ridha mai aniya

Fari ya zazzago dukan isnadi
Har Ma'aiki ya dangana ba tawaya

Ya kwa godewa Rabbana da iyaye
Malamai har da yan uwan zurriyya

Za na kwan yau farin ciki da nishadi
Dalibina cikin sahun yan manya

Nan na ke kare baitukan taya murna
Gunsa Musa da sha-bakwan jeranya

Da ace babu masu koyo tabbas
Da gwanayenga za su zam jin kunya

Yau Jumada Na Sani ya kai shidda
A alif sai ɗari huɗu ka ƙidanya

Arbain sai ukun da za kai ƙari
A ƙidayar mu ai nufi Hijriyya

Lahadin ce tara wata na Janairu
A dubu biw twenty-two Girigiyya

Ni Bashiru Uban Humaidah Na tsara
Ala sa nai ta ne da kyawun niyya

Hamdala gun Gwani, Hakeem Rahmani
Sai salati akan Uba ga Ruƙayya

Comments

Popular posts from this blog

Raina Fansar Ka

BARAM-BARAM

Ya Rabbana raya mana Muhammada