DUBORA INA UMMU.QABEEH?

Banga ribar ja'irai ba

Masu zagin Shugaba ba

Ɗaukaka girma da haiba

Rabbana Mahmudu yabba

Masu ƙinsa a hir ku daina gaba

Inko kunƙi ku daina walla

Za ku saura ku na ta ƙwalla

Har fushi ya kashe ku zalla

Mujtaba zaɓi na Jalla

Mai ƙinsa ba zai ga fa'ida ba

Da a Denmak ko Faransa

Ne mu ke jin masu ƙinsa

Na ta barkwanci da wasa

Wanda ke taɓa janibin sa

Ba mu yarda da wagga shaiɗana ba

Ga Yahudu haɗa Nasara

Harda arne mai tsirara

Bai da aiki sai harara

Martabar Manzon mu Nura

Yin hakan bai tauye martabar ba

Babu alfahri batun nan

Shugaba ne gun mutanan

Can na farko har zuwa nan

Ƙin ku koko son batun nan

Haka dai yake bada gardama ba

Arniya a garin na Shehu

Ta yi ɓanɓarma da ihu

Kan Fiyayyen nan Fasihu

An baje ta su na ihu

Ba mu san manufarsu duniya ba

In tace Isah Na kowa

Wai Ɗayan Uku ne da sowa

Har ta nemo amsa kuwwa

MA BIHI KAFARAT ta zowa

Ba ruwan mu ba za mu kai ido ba

Wanda yattaɓa Shugaban mu

Ba mu ji kuma ba gani mu

Kansa duk mun bada ran mu

Don mu fanso Shugaban mu

Ban ji mai zaginsa ya haye ba

Munji Alƙali Iyalu

Ya faɗa kuma ga dalilu

Wanda yattaɓa Ɗan Halilu

Sai kisa ba sauya ƙaulu

Tuba bai sauya yin hakan ba

Sai a bar shi a gun hakuma

Don gudun tashin husuma

Bincike ita za ta soma

Kar ya zam an bada dama

Ai hukunci ba da tabbaci ba

Koda dai na san mutane

Nada shakku kan abunne

Kan batunga na Abdu Wane

Wanda yai zagi Kano ne

Shi ya sa ba su bar ta ta ware ba

Kai ko mai sukan hukunci

Ai kisan duk wanda yacci

Duk mutuncin Mai Aminci

Don ka burge ko tukuici

To ka tuba ka zam biɗa ga Rabba

Rabbana tuba mu ke yi

Kan abinda wasun mu ke yi

Keta alfarmar Nabiyyi

In azaba za ka zam yi

Ka tsare mu fushinka don na Garba

Kai salati har salami

Ƙan sa Manzon nan Imami

Shugaba Badarut-tamami

Kunji mai yaye gumumi

Sarmadan ƙaunar sa ban tsaya ba

Comments

Popular posts from this blog

Raina Fansar Ka

BARAM-BARAM

Ya Rabbana raya mana Muhammada