BONE KAN KU

Jafa'i kan ku Denmak ke da Nowe

A kan gauƙan da kun kai kui hawawe


Ace Manzon da babu kamar s akwata

Ku ke wa ba'a fa kun san kunyi wauta


Ina zatgin ku zargin bai zaya ba

Ina zagin ku zambo ban raga ba


Akan ƴanci na furci sun ka yo wai

Da farko har da arnan sun ji bawai


Ama manyan musulmiya kona oho

Fa sai ƴan kasuwa ne sun ka eho


Suna Allah wadai kan wanga assha

Musulmai hankali duk ya yi tsahi


Ina.wai duk ƙasashen masu fetur

Musulmin nan cikin su su dinga tur-tur


Fa fetur na mu ba shi zuwa ga Denmak

Ku bar Dolar ku, Sefa koko Dochmak


Kaza dukkan ƙasashen nan na yamma

Akan cutar mu kullum su ka yimma


Fa ranar duk musulmi sun yi shewa

Gama kalmar Ta'ala tai ɗagawa


Daɗewa Ali Mazrui ya yi sharyi

Akan shi feturi Allah Buwayi,


Ya na jibge shi ne gun duk ƙasashan

Musulmai koko inda su kai yawa shan


Makammin nan da Allah yaffa ba mu

A ya zarce su nukiliya a gun mu


Musulmi na kiran duk masu ilmi

Na sadarwa ku tashi ku dinga ƙaimi


Akan radɗi ga arna masu bante

Su na yawo kanar talbal-batete


Idan sunce kule sai kui ta cas cas!

Cikim hikima da wa'azi cancaras cas


Tsiraru ne fa sai zaƙi na.baki

Muƙunshin gisshiri kam ya fi zafi


Musulmi gun yawa in su dubu ne

Dubu biyu za su kora ko da ja ne!


A yau mun zan fa taron tsintsiya ne

Da ba shara a hir to za.mu ƙone


Ina ta kiran musulmi ƴan uwana 

Mu tashi mu bar kasala har da kwana


A yau tsari na jari ne fa hujja

Mu ce a'a ga dukkan tasu haja


Da hudawa jini ne anka tadda

Da son afwa fa sun aiko takarda


Ama laifin da sun kai ya ƙazanta

Fa ba afwa a sannan ba nu manta


Ilahi Annabin ka ka yo wa hakka

Fa ɗaman alƙawar kai tun a Makka


Na kare izgilancin masu shirka

Akan Manzo Muhammad Annabin ka


Ta'ala ga su nan kuna kana ga ka

Kayo damƙa irin wannan fa taka


Da ƙarfi gun ka na san babu shakka

Fa kafircin su sam bai gagarar ka


Daɗo tsira darajja har karmci

Bisa Manzon ka Ahmadu har aminci


Ka yi musu yanda kai wa kafirawa

Na farko inda ƙari kai daɗawa


Kamar Ɗufana kan jama'a ta Nuhu

Da iska kan Samudu su dinga ihu


Da tsawar nan guda ɗai kan Samudu

Da kantafin kifarwar Alu Luɗu


Ka mai da saman su shi ne ƙarƙashin su

Ka bi du da damima ta ruwan duwatsu


Ka yi musu yanda kaiwa mutan Shu'aibu

Da ke tauye shi mudu sun yi aibu


Ka kai su tsakan ruwa sannan ka shafe

Kamar Fir'auna masu riƙon madafe


Ka aiko dandazon tsuntsu-duwatsu

Kamar mahayan na giwa sui kisan su


Ka aiko dukkanin narkom azaba

Haɗo har wadda ni ma ban sani ba


Gama ka shafe arnakun gaban su

A ƙarfi har da ƴaƴa dukiyar su


Kaza tarin gidaje har sanin su

Ama yau sai kawai tatsuniyar su


Haɗa har duk ƙasa mai goya baya

Da wanda akan batun ma ke ta kunya


Haɗe har majlisan nan ma ta Niwyo

Game har karnukan su walau a Auyo


Ka aika ruwa tsunami ya dinga bori

Amam dutse da zalzal masu tsauri


Ka sa yunwa, fari duk lardunan su

Kaza yaƙinda cuta addabar su


Musulmi na yi jaje duk a gun ku

Makoki ne muke kam babu shakku


Mu dage addu'a ita ce makami

Mu ɗau keyboard da raddin nan na ilmi


Ayo raddi duhun nan duk mu yaye

Gama dunyar a yau ta zam ya ƙauye


Akan wannan fa rana za ta kisfe

Ya zamto wanga haske ya fa shafe


A ran ashirin tara ga wata na Marshi

Ya maimaito azabar nan ta lumshi


Kusufi anka yo don razanarwa

Da cewa Jalla shi sam bai macewa


Mu san girman sa Manzo ya fi komai

Cikin ƙassai haɗa duk har da sammai


Salati kan sa mai kamshi da.haske

Da duk wani mumini mai ba shi sulke


B.I Unar

13/Muharram/1427

11/2/2006

Digitalized on: 12/9/2023

Comments

Popular posts from this blog

BARAM-BARAM

MAWADDAH

Raina Fansar Ka