MUHAMMADU YA FI KOWA

YA FI KOWA! YA FI KOWA! YA FI KOWA!

A yau kuma zan Safa ne har da Marwa

Akan duk masu karyar wallafawa

Taqiyyar son fiyayyen Annabawa

Da bai iya son sa har ya ji ya fi kowa


Akwai wasu sun amai sai sunka lashe

Mu na nan har jinin mu diga ta ƙarshe

A tsarin kare Manzo Ɗan Abashe

Da cewa duk halittu ya fi kowa


Idan kai ba ka yi to ba mu fili

Batu kan martabar jikan Khalili

Muhammadu Mujtaba Yayan Aqili

Mu na kai har mu koma can kushewa


Faɗan nan ba na mai tsoro ba ne ba

Idan za kai ka jure duk azaba

Anan dunya a can ko duk da riba

Fa sai dai ɗan kucaki bai iyawa


Idan na tuno guruf ɗin ƴan hakika

A shafin Facebook don yaɗa shirka

Da daukaka shehinai kan Masu Makka

Takaici har hawaye nai zubarwa


Idan kun tsuke baki ni ku ji ni

Ba zanyi shiru ba ko zan karɓi tsini

Takobi, tsitaka mashi biyo ni

A tsagin kare Manzo ban gazawa


Idan ka ji wanga waƙe kaffusata

Munafunci da tsatsa sun yi kanta

A ƙoƙon zuciyar ka idan na keta

A ƙaunar Mustapha ban ratsa kowa


Idan ka ji ka fi son wani kan Muhamman

Ka san cewa da saura gun ka malam

Hadisin Faruku duba musamman

Wajen AL-ANA kai kaiwa da jewa


Idan wani ya faɗi to za ni ƙara

Na ƙara fade a waƙe ma na rera

Ma'aikina da shi ne zan gadara

Ta cewa duk halittu ya fi kowa


Idan haka ba shi yi ma sai ka doɗe

Asusuna idonka ya na a buɗe

Gama na san yawanci za su ruɗe

Fa Mark ya ba da damar garƙalewa


Fa Ahmadu ya zamo zaɓi na Allah

A tun Ranar ALASTU da anka shela

Ya amsa kan BALE Manzo Rasula

Gaban kowa Ilahu ya ba shi baiwa


Muƙamin nan azal ne ba bu sauyi

Wajen bautar ka ko naci ka ke yi

Ba za ka matso matakin shi Taqiyyi

Muhammadu ya wuce har yai ƙulewa


Idan ranar qiyama anka tashi

Anan ne za ku ƙara sanin irin shi

Wajen ceton da Allah za ya ba shi

Haƙiƙa shi ya zam rahma ga kowa


Da shi ne za'a sa mudun hisabi

Abinda mu kai yaƙini nan da gaibi

A ware ƴan Na'imu da ƴan azabi

Waɗancan na ta kuka mu ko shewa


Da alƙawarin da Allah yai wa Manzo

Na cewa za ya ba shi haɗi da bozo

A ranan nan da ke dako da ta tazo

Idan Allah ya ce bai warwarewa


Fa zai ceto ga duk mai bin sa tabbas

Ma'aiki ne isasshe ɗa ga Abbas

Ta'ala shi ya tsara shi ya zaɓas

A bar yin ja da cewa ya fi kowa


Muhammadu ya fi kowa ya fi kowa

Fa zan ta fada da gunji ba tsayawa

A ko yaushe ku ji ni Muhammadawa

Batun nan ko ba zai daɗi ga kowa



Comments

Popular posts from this blog

BARAM-BARAM

MAWADDAH

Raina Fansar Ka