SARKIN SARAKUNAN TAUSHI (Hassan Ɗan Thabit)

Farko da sunan Gwani wannna da yai iska

Roƙon da nayyi ka ban ilmi na domin Ka

Sannan ka ba ni fasaha yanda zan taka

Rawar da ba muguwa ba wajen yabon na Ka

Da shi da dukka sahabban Sidi mai Makka


Allah Gwani na Muhamman inji kakata

Ƙaro dami na salati kan Uban Binta

Alai sahabbai da ƴaƴa har da mai bauta

Bautar Ta'ala da yai Gano da Ɗanbatta

Har masu bin su da kyawu ba su yin shirka


Bayan hakan zan bayanin Mai kiɗan taushi

Hassanu mai kare Manzon nan Maje Arshi

In an taɓa shi ya zam zaryar da ba fashi

Zai kai mari har da gwauro don ya wanke shi

Hassanu Kam ya rabauce babu ko shakka


Kafin zuwan Islama ya zamo gwarzo

Harshensa kansakali mai fauce duk zozo

Zai sulluɓe su da baitoci ya duddurzo

Jinga ake yi da shi gayya idan sun zo

Domin ya kare ƙaɓilu tun ana shirka


Ana cikin haka sai Manzo ya zo da kira

A daina bautar gumaka don a san tsira

Arna su kai dandazo har ma su na kyara

Ga Shugaba na halittun nan Uban Zahra

Hassanu shi ma a loton na cikin harka


Sun tattago shi ya je wai don ya yo nazari

Domin ya san yanda zai zambo ga Albashari

Yayinda yagga Rasulullahi yai marari

Jazba ta kama mawakin har ya na ta ɓari

Baitin yabo ga Rasulullahi Mai Makka


Nan ne ya saƙa kasidar nan ta tasshara

Wannan da ke yi cikin shauƙin cikin halara

Kyawun Ma'aiki ya ce dunyar ga bai tsara

Ya ce Ma'aikin kamar shi yai wa kan sa dira

Sannan yace ba uwar da ta haifi tamkar ka


Da ga nan ya bayyana Imani ya daina sake

In za su je su gumurzu sai ya dau silke

Ya ce ku bar kansakal domin da baki na ke

Hassanu ke ta shiga tsakiya ya na ta cake

Ya na kirari ga Manzo har sahabu duka


Wataran ya ce da Ma'aikin so na ke na zamo

Mai baka duk kariya har ma na kai komo

Kan dukkanin masu cutarwa da sun zarmo

In sun yi zambo ya zamto ni nake ramo

Abinda duk su ka ce kan Sidi mai Makka


Ya ce da shi je ga Siddiq ko na ce Garba

Domin ko shi a Ƙuraishin kwai sanin nasaba

Domin gudun kar wajen sukar su ƴan gaba

Ka je ka sanya da ni Abba ga Zainaba

Don kakanin mu guda ne su su kai shirka


Hassanu nan ya faɗa zan fidda kai Mahi

Tamkar fita da zaren gashi cikin mayhi

Nan ne Ma'aiki ya roƙa mas haɗin Ruhi

Jibrilu mai ƙarfafa da nufi na Lillahi

Ya san rabauta dalilin kare mai Makka


Duk masu bege yabo ga sarakunan dunya

Ba wanda yayyi gamo na katar matso ku jiya

Tamkar su Hassanu sarki mai kiɗan shiriya

Ranar ƙiyama ina son za ni mai rakiya

Girman abinda ka bega shi ya nashe ka


Allah ya ba mu ya taku ba mu kaiwa ku

Na so na zamto ina bin inda kai taku

Fannin yabon Mujtaba ku kun zamo teku

Wa za ya kalle mu in an ce a yau ga ku

Hassanu ƙaunar ka ni zan yi ta ba shakka


Yarda ta Allah a kullum za ta ƙaru ga shi

Domin Ma'aiki na Allah ya kwa yarda da shi

Allahu sanya mu tashi gaban Maje Arshi

Ya dinga zabga yabon mu ko mu na amshi

Allahu amsa du'ain don sa mai Makka


Tsira aminci na Allah kan sa Manzon mu

Ƴaƴa, sahabbai da mataiku iyayen mu

Har masu bin su da kyau hanyar su sun kamu

Ga malamai ƴan uwa ka haɗa iyayen mu

Ya zamo a ranar ƙiyama mun wuce duka




Comments

Popular posts from this blog

BARAM-BARAM

MAWADDAH

Raina Fansar Ka