WA YAI KAMA TASA DUK BAYI NA RAHMANU?

Wa yai kama tasa duk bayi na Rahmanu
Ra'ufu ne da Rahimu jini na Adnanu

Bismillah Sarki Gwani Rahimu Rahmanu

Ka ba ni himma cikin bege na Ma'munu


Tsira hada da aminci kan sa Miftahu

Haɗa da albarkatu jinkai na Hannanu


Saka ciki alihi har duk sahabbansa

Da ma su bin su da kyawu duk cikin kaunu


Na ɗauki allo na latarki Ina da nufin

Tsaro yabo a wajen suriki na Usmanu


Na firgice ni a ƙaunar nan ta Manzon mu

Wasu lokutan ma Ina jin na fi majnunu


Riba ta begen Rasulullahi ba ta Sa'a

Duba ga ƙissa ta Ka'abun nan da Hassanu


Yayin da Manzo ya sa neman ruwan jallo

Gun Ka'bu bi ni gaba zan ba ka duk kanu


Zambon da yai wa Ma'aikin ne ya sanya Hakan

An sa a Nemo shi ko da har cikin bunu


Sai ɗan uwansa ya je ya sanar da shi halin

Da ake ciki a gari halin da yai munu


Amma ya ce masa shi Manzon maji ƙai ne

Ga yafiya a wajen Bawan na Rahmanu


A cikin duhu na dare kafin kiran fajaru

Ya je ya kai shi gaban Manzo ya gurfanu


Nan ne ya buɗe kasidar nan da tasshara

BANISSU'ADU da ke bege ga Ma'munu


Daɗin yabon nan ya sanya Ɗaha yayyafe

Har ma ya ba shi tukuici Shugaban Kaunu


Kwai inda ma a yabon Manzo ya mai darasu

Kan babu wai shi takobi ne na Dayyanu


Nan Kun ga inda yabon Manzo ya cece shi

Bayan da anka halsata jinin na Ɗan Qainu


Yabon sa ya zam silar tsira wajen Ka'abu

Haka nan idan kun tuno ƙissa ta Hassanu


Begen ka shi na rike nima Ina da nufin

Samun kusanci da kai ran auna mizanu


Ni ba sani a wajena ba yawan zikri

Amma ina son ka ƙauna babu tammanu


Begen ka shi na rika matsayin wuƙar ƙugu

Domin na samu shiga ƙofa ta Rayyanu


Ni ban yawan azumi kuma ba yawan sallah

Begen ka zai sa na san tarba ta Rilwanu


Manzo Muhammadu dunya ban da tamkar ku

Ahalin ka sanya da ni tamkar ta Salmanu


Rokan na san hikima tamkar ta Hassanu

Wajen yabon ka na san matsayi na sultanu


Shi ne ya san karfafawar Ruhu ba shakka

Tamkar ta Isa na Maryam don yabon na ka


Ni.ma a zam ƙarfafa ta nai ta begen ka

Ba gargada ko guluwwi don su Adnanu


Farfajiya ta ƙiyama sa a nemo ni

Domin na buɗe yabon suriki na Usmanu


Zambar dubu ta salati Jalla mai Iko

Dado su kan Mahmud jika ga Adnanu


Allah da duk malakutu su na salatinsa

Kui sallama da salat in kun yi imanu










Comments

Popular posts from this blog

BARAM-BARAM

MAWADDAH

Raina Fansar Ka